BUA Ya Sanar Da Ƙarawa Ma’aikatansa Albashi Kashi 50 Cikin 100 Saboda Tsadar Rayuwaby Muhammad


ADVERTISEMENT


Shugaban Kamfanin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya ce kamfanin ya amince da karin albashin ma’aikata kashi 50 cikin 100.

Rabiu ya bayyana hakan ne a cikin wata takarda ta cikin gida da shugaban ma’aikata na BUA, Mohammed Wali, ya sanya wa hannu ranar Lahadi a Legas.

Sanarwar ta ce, shugaban BUA ya ce karin kudin an yi shi ne don rage radadin matsin tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta a halin yanzu.

Ya ce karin albashin zai shafi ma’aikata na dindindin/da na wucin-gadi zai kuma fara aiki daga ranar 1 ga Fabrairu, 2024.

“Ana fatan da wannan gagarumin karimcin, zai sa mu kara himma wajen gudanar da ayyukanmu tare da yin iya kokarinmu don tabbatar da irin kwarin guiwar da aka yi mana,” in ji shi.

Comments

Popular posts from this blog

Sojojin Najeriya sun kashe 'yan bindiga a Neja da Borno

HOTONAN Yadda Kabilar Dakarkari ke cigaba da gudanar da wasannin al'adun Gargajiya Zuru Uhola.

Babban Zauren MDD ya nemi Kwamitin Sulhu ya amince da ƙasar Falasɗinu