Posts

Showing posts from February 8, 2024

Majalisar wakilan Najeriya za ta ƙarfafa dokar ɓata-sunaKakakin majalisar wakilan Najeriya,

Image
Tajudeen Abbas ya ce majalisar za ta ƙarfafa dokar ɓata-suna da cin cin mutuncin mutane da kuma cin zarafin mutane ta intanet. Honarabul Tajedeen ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai kan abubuwan da ke damun ƙasar da aka gudanar a wani ɗakin taro a harabar majalisar. Kakakin majalisar ya ce manufar dokar ba zai ci karo da 'yancin faɗar albarkacin baki, amma za ta kare mutane da hukumomi daga cin zarafinsu a intanet. Ya ƙara da cewa dole ne 'yan Najeriya su damu bisa yadda ake yawan cin zarafin jami'an gwamnati a shafukan intanet. Honarabul Abbas ya bayyana yadda kakakin majalisar da ya gabace shi, Femi Gbajabiamila, ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka fuskanci cin zarafi da intanet, da ɓata suna

NNPCL ya musanta shirin ƙara kuɗin man fetur

Image
Getty Images Copyright: Getty Images Kamfanin mai na Najeriya NNPCL ya musanta duk wani yunƙuri na ƙarin farashin man fetur a faɗin ƙasar. A baya-bayan nan masu ababen hawa na fuskantar dogayen layuka a wasu gidajen mai a wasu yankunan ƙasar, musamman a kudancin ƙasar, sakamakon fargabar da ake yi cewa hukumomi za su ƙara farashin man. To sai dai a cikin wata sanarwa da kamfanin mai na ƙasar, NNPCL ya fitar mai ɗauke da sa hanun jami'in hulɗa da jama'a na kamfanin, Olufemi Soneye ya fitar, ya buƙaci 'yan ƙasar su kwantar da hankalinsu. ''Ba za a ƙara kuɗin man fetur ba'', kamar yadda sanarwar kamfanin ta tabbatar. “NNPC Ltd na buƙatar 'yan Najeriya su yi watsi da duk wata jita-jita da ta dangancin ƙarin kuɗin mai, kuma kamfanin na son tabbatar wa 'yan ƙasa cewa babu wani yunƙuri da hukumomi ke yi game da ƙarin kuɗin man'', in ji sanarwar. Tun bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin ƙasar ta yi cikin watan Mayun shekarar da ta gabata, faras