Posts

Showing posts from February 7, 2024
Image
  Gazawa ce APC ta fito tana zargin ƴan'adawa" ASALIN HOTON, FACEBOOK/ATIKU ABUBAKAR/PETER OBI Sa'o'i 3 da suka wuce Jam'iyyun adawar Najeriya sun mayar wa APC mai mulki martani, kan zarginsu da hannu wajen tunzura jama'a domin yi wa gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu bore. Lamarin ya biyo bayan zanga-zangar da aka gudanar a jihohin Kano, da Neja da Legas, kan tsadar rayuwa. Sai dai a cewar jam'iyyun adawar jama'iyyar APC ce a kan mulki, don haka alhakin tabarbarewar lamurra a kasar ya rataya ne a wuyanta. Manyan jam'iyyun adawar Najeriya PDP da LP, sun ce cunar rigar jam'iyyar APC ce ke neman kayar da ita, kuma tun farko kankanba ce ta kai ta ga neman sahalewar 'yan Najeriya domin jagorantarsu, ba tare da wani tartibin tsarin yaye musu matsalolin da suke ciki ba. TALLA Shi ya sa a yanzu bayan shafe kusan shekara guda a kan Mulki da shugaba Tinubu ya yi, take zarginsu da yi wa gwamnati shune, kamar yadda jam'iyyun biyu suka bayyana. Mat