Posts

Showing posts from February 1, 2024
Image
 Sadio Mane: “Ina mai baki haƙuri Mata ta, Bazan iya kawo miki kofin da kika buƙata a matsayin kyautar Auren mu ba, Nayi iya bakin ƙoƙarina amma hakan bai wadatar na samu kofin ba ina mai baki haƙuri.”

labarai suna tambayar ‘Wai me yasa har yanzu ba a ga Ahmed Musa a cikin fili ba’. Kamar

Image
 labarai suna tambayar ‘Wai me yasa har yanzu ba a ga Ahmed Musa a cikin fili ba’. Kamar yadda kuka sani wannan ba sabon abu bane. “Komai nufi ne na Allah, Idan Allah yaso Ni zan shiga na sauya wasa. Ko kuma Ni zan kawo sakamakon abun da ake nema shikenan, Kawai ni fata na a cigaba da yimin da kuma ƙungiyar mu Addu'a duk mai haƙuri yana tare da samu. “Nasara muke buƙata duk wanda yake cikin fili indai yanayin abun da Yakamata to mu bashi goyon baya. Duk randa Allah yayi na shigo kuma na zama silar naasarar mu hakan shine rabo na, Kuma babu wanda yake tsallake wa rabon sa.” - In ji - Ahmed Musa Kyaftin ɗin Super Eagles a zantawar sa da RFI Hausa.  

EFCC na bincike kan yarjejeniyar Nigeria Air - Keyamo

Image
Copyright: Nigerian Govt Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya Festur Keyamo ya ce hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Najeriya EFCC na gudanar da bincike kan yarjejeniyar kamfanin jiragen sama na ƙasar wato 'Nagerian Air' mai cike da ce-ce-ku-ce da gwamnatin tarayya ta ƙulla ƙarƙashin tsohon ministan kula da sufurin jiragen sama na ƙasar Hadi Sirika Yayin da yake zantawa da gidan talbijin na Channels ranar Laraba, mista Keyamo ya ce “EFCC na bincike kan yarjejeniyar. ''Ana gudanar da bincike kan lamarin, kuma muna jiran rahoton binciken''. Mista Keyamo wanda suka yi aiki tare da Siriki a matsayin ministocin gwamnatin Buhari, ya ce babu wani kamfanin jirage da ke aiki a matsayin kamfanin jirage na ƙasa, amma ya ce za a samar da nagartaccen kamfanin jirage na ƙasa. A watan Agustan bara ne Mista Keyamo ya ƙaryata yarjejeniyar da Sirika ya ƙulla tare da dakatar da duk wani shiri da ke cikin yarjejeniyar. Batun yarjejeniyar kamfanin 'Nigerian Air' da

Kungiyar dattawan arewacin Najeriya da takwararta ta Ohanaeze Ndigbo mai kare muradun al'ummar Igbo da wasu kungiyoyin farar hula sun bayyana rashin jin dadinsu game da tafiya zuwa Paris da shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi daidai lokacin da kasar ke fama da karuwar matsalar tsaro.

Image
 Kungiyar dattawan arewacin Najeriya da takwararta ta Ohanaeze Ndigbo mai kare muradun al'ummar Igbo da wasu kungiyoyin farar hula sun bayyana rashin jin dadinsu game da tafiya zuwa Paris da shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi daidai lokacin da kasar ke fama da karuwar matsalar tsaro. A ranar Laraba 24 ga watan Janairu ne shugaba Tinubu ya tafi zuwa Faransa domin wata ziyara ta kashin kai. Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Ajuri Ngelale ya fitar gabanin tafiyar, ta ce Tinubu zai koma Najeriya cikin makon farko na watan Fabarairu. Sai dai kungiyoyin a hirarsu da jaridar Daily Trust sun koka cewa babu gaskiya cikin sanarwar tafiyar la'akari da yadda aka kira tafiyar ta "kashin kai". Matakin kungiyoyin na zuwa ne bayan da shi ma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya soki Tinubu inda ya bayyana shakku game da makasudin tafiyar tasa zuwa Faransa yayin da ake fuskantar karuwar matsalar yan bindiga da sauran matsalolin tsaro da ke ci gaba da ta'azzar