Posts

Showing posts from February 4, 2024

Dakarun Najeriya sun kuɓutar da mutane daga hannun masu garkuwa a Taraba b

Image
  Kanawa post news  Rundunar sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu jami'an tsaro, sun lalata wata maɓoyar masu garkuwa da mutane tare da kuɓutar da mutum huɗu da aka yi garkuwa da su a yankin ƙaramar hukumar Yorro na jihar Taraba. Cikin wata sanarwa da mai riƙon muƙamin daraktan yaɗa labaran rundunar sojin Najeriya ta 6 da ke jihar, Laftanar Oni Olubodunde ya sanya wa hannu, ya ce sojojin sun ƙaddamar da yaƙi da 'yan bindigar ne tun da suka yawaita kai hare-hare a yankin ƙaramar hukumar. Ya ƙara da cewa dakarunsu sun yi gumurzu da masu garkuwar a tsaunukan Gampu da na Ban Yorro, bayan musayar wuta tsakanin ɓangarorin ne, sai 'yan bindigar suka arce inda suka bar mutum huɗu da suka yi garkuwa da su. Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin za su ci gaba da aiki a yankin har sai sun tabbatar da kuɓutar da sauran mutanen da ke hannun masu garkuwar.

Tinubu ya aike da ta'aziyyarsa kan rasuwar shugaban Namibiya

Image
Bola Ahmed Tinubu/XCopyright: Bola Ahmed Tinubu/X Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyyarsa ga al'ummar Namibiya bisa rasuwar shugaban ƙasar Hage Geingob. Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale ya fitar, shugaba Tinubu ya ce ya kaɗu da jin labarin rasuwar mista Geingob, wanda ya bayyana da ɗan kishin gwagwarmayar tabbatar da dimokraɗiyya. Shugaban na Najeriya ya kuma bayyana marigayin da jagoran tabbatar da jagoranci nagari, da bunƙasa tattalin arziki da ci gaba al'ummar Afirka. Shugaba Tinubu ya ce marigayin ya rasu ne a daidai lokacin da nahiyar Afirka ke buƙatar jajirtattun shugabanni irinsa, waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen bunƙasa nahiyar ta ko wanne fannin ci gaba. Daga ƙarshe shugaba Tinubu ya ce a madadin gwamnatinsa da al'ummar Najeriya suna miƙa saƙon ta'aziyyarsu ga ɗaukacin al'ummar Nambiya bisa wannan babban rashi da suka yi. Hage Geingob: Shugaban Namibia ya rasu yana dan shekara 82 Article

Mayakan ISWAP sun kashe 'yan sanda hudu a harin da suka kai a Borno

Image
G NPFCopyright: NPF Aƙalla 'yan sanda hudu ne suka rasa ransu sannan aka kwashe dimbin harsasai masu yawa a wani hari da ake zargin mayaƙan ISWAP ne suka kai ofishin 'yan sanda a Ƙaramar Hukumar Nganzai da ke Borno. Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mayakan ISWAP sun kutsa kai ne cikin ofishin 'yan sandan tare da buɗe wuta kan jami'an da suke aiki. A cewar majiyar tsaro, mahairan sun ƙona wani ɓangare na ofishin 'yan sandan lokacin da abin ya faru a ranar Juma'a. "An samu ruɗani a garinmu a daren jiya. MMayaƙan ISWAP sun kai wa ofishin 'yan sanda hari a Gajiram. Kuma gaskiya sun fi ƙarfin jami'an da suke kan aiki." "Mun samu gawar 'yan sanda hudu a yashe a inda abin ya faru da safiyar yau, har yanzu ba a ga wasu 'yan sandan da suka tsere ba," in ji wani jami'in 'yan sa-kai. Rahotanni sun ce maharan sun bar wurin tun gabanin sojoji su isa.