Posts

Showing posts from February 19, 2024

Kamfanin AEDC ya yi barazanar yanke wa fadar shugaban Najeriya wutar lantarki

Image
PRESIDENCY NG Copyright: PRESIDENCY NG Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu Image caption: Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu Kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja AEDC ya yi barazanar katse wutar lantarki a fadar shugaban Najeriya da na wasu ma’aikatun gwamnati 86 a kan bashin kuɗin wuta sama da naira biliyan 47 da yake bin su. Wasu daga cikin ma'aikatun da barazanar ta shafa sun haɗa da ma'aikatar kuɗi da ta yaɗa labarai da ta kasafin kuɗi da ta ayyuka da gidaje, da gwamnan CBN da ofishin Hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) da sauran su. A cikin sanarwar da kamfanin ya fitar a ranar Litinin, AEDC ɗin ya bai wa ma'aikatu da ofisoshin na gwamnati kwana 10 domin biyan basukan ko kuma a yanke musu lantarki, wato daga 28 ga watan Fabarairun 2024. Bangaren samar da wutar lantarki a Najeriya dai ya shafe shekaru yana fama da matsalar bashi. A makon da ya gabata ne Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya ce umarci kamfanonin rarraba wutar lantarki (DisCos) da su t

BUA Ya Sanar Da Ƙarawa Ma’aikatansa Albashi Kashi 50 Cikin 100 Saboda Tsadar Rayuwaby Muhammad

Image
ADVERTISEMENT     23 hours ago Shugaban Kamfanin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya ce kamfanin ya amince da karin albashin ma’aikata kashi 50 cikin 100. Rabiu ya bayyana hakan ne a cikin wata takarda ta cikin gida da shugaban ma’aikata na BUA, Mohammed Wali, ya sanya wa hannu ranar Lahadi a Legas. Dalilan Da Suka Sa Har Yanzu Ba A Rage Farashin Simintin BUA Ba Bayan Rage Farashin Siminti, BUA Ya Kara Farashin Suga, Fulawa Da Taliya Sanarwar ta ce, shugaban BUA ya ce karin kudin an yi shi ne don rage radadin matsin tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta a halin yanzu. Ya ce karin albashin zai shafi ma’aikata na dindindin/da na wucin-gadi zai kuma fara aiki daga ranar 1 ga Fabrairu, 2024. “Ana fatan da wannan gagarumin karimcin, zai sa mu kara himma wajen gudanar da ayyukanmu tare da yin iya kokarinmu don tabbatar da irin kwarin guiwar da aka yi mana,” in ji shi.

Za Mu Ɗauki Mataki Kan Duk Masu Sukar Shugaba Tinubu Kan Tattalin Arziƙi – Bello Matawalle

Image
by   Muhammad     12 seconds ago Labarai Masu Nasaba Gwamnatin Katsina Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Aiwatar Da Dokar Hana Boye Hatsi Da Tsadar Haya BUA Ya Sanar Da Ƙarawa Ma’aikatansa Albashi Kashi 50 Cikin 100 Saboda Tsadar Rayuwa   Ƙaramin Ministan Tsaron Nijeriya ya yi tsokaci kan koke-koken da jama’a ke yi kan matsin tattalin arziki da ƴan kasar ke fama da shi a yanzu haka. Jaridar yanar gizo ta ‘ Tarayya ’ ta yi karin haske kan cewa, a cikin wannan shekarar, wasu fitattun ƴan Nijeriya, ciki har da Sarkin Musulmi Sa’ad Abubakar III da Sarkin Kano Aminu Ado Bayero da shahrarren lauya Femi Falana sun bayyana rashin jin daɗinsu da halin da ƴan ƙasar suko A makon jiya kuma, ƴan Nijeriya sun yi zanga-zanga a jihohin Neja da Kano da kuma Legas kan matsin rayuwa da suke fuskanta. Gwamnatin Bola Tinubu ta ce tana ƙoƙarin warware matsalar ta hanyar raba kayan abincin da ke rumbunan gwamnati, sannan ta ɗora laifin taɓarɓarewar tattalin arziki kan tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari.