Posts

Showing posts from March 4, 2024

Barcelona ta sake yin tuntuɓe a La Liga

Image
Barcelona ta kasa cin gajiyar sakamakon sauran wsasannin da suka gudana a gasar La Liga bayan da ta yi canjaras 0-0 da Athletic Bilbao wanda hakan ke nufin ta ci gaba da kasancewa a matsayi na uku a kan teburi. Yayin da Girona da ke matsayi na biyu ta sha kashi a hannun Mallorca, Barcelona ta samu damar ɗarewa kanta a teburi idan ta yi nasara, amma Bilbao ta tabbatar da hakan bai faru ba. Yayin da Barcelona ke shirin fafatawa da Napoli a wasan zagaye na biyu na gasar cin kofin zakarun Turai ranar 12 ga Maris, kocin Barcelona Xavi ya shiga tsaka-mai-wuya yayinda Frenkie de Jong da Pedri suka bar filin wasa da raunuka. Sakamakon wasan dai ba yi wa kowanne ɓangare daɗi ba inda Barcelona ta maƙale a matsayi na uku da tazarar maki takwas tsakaninta da Real Madrid. Ita kuma Athletic Bilbao da ke matsayi na biyar ta ƙara samun koma baya a yaƙin neman matsayi na huɗu a teburin gasar inda ta samu kanta da tazarar maki biyar tsakaninta da Atletico Madrid wadda ta doke Real Betis da ci 2-1.

Za mu tsaurara tsaro a rumbunan ajiye kayan abinci - NEMA

Image
Hukumar kai ɗaukin gaggawa ta Najeiya (Nema) ta ce za ta tsaurar tsaro a rumbunan ajiye kayan abincinta da kuma ofisoshinta da ke faɗin Najeriya domin kare su daga 'ɓata-gari’ Hakan na zuwa ne bayan harin da aka kai kan wani daga cikin rumbunanta da ke Abuja, babban birnin ƙasar a ranar Lahadi. Wasu matasa ne ake zargin sun kai farmaki kan rumbun wanda ke unguwar Gwagwa da ke birnin na Abuja, inda suka yi awon-gaba da kayan abinci da kuma sauran abubuwan da aka taskace a rmbun. Wata sanarwa da ta samu sa hannun mai magana da yawun hukumar ta NEMA, Manzo Ezekiel, ta ce "Shugaban hukumar na ƙasa, Mustapha Ahmed ya bayar da umarnin a tsaurara tsaro a ofososhi da kuma rumbunan ajiye kayan hukumar a faɗin Najeriya domin kauce wa kutsawa cikin su." Najeriya dai na fama da matsi na tattalin arziƙi, inda mutane da dama ke kokawa kan rashin abinci da tsadar kayan masarufi. Kafin fasa rumbun ajiye abincin a Abuja, an samu rahotannin yadda mutane suka far wa motocin dako