Posts

Showing posts from February 2, 2024

Muna da ƙwarin gwiwar doke Angola - Ekong

Image
  ASALIN HOTON, GETTY IMAGES Bayanan hoto, Najeriya za ta buga wasanta na 11 a matakin daf da na kusa da na ƙarshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka - babu wata ƙasa da ta kai ta buga wasanni a wannan mataki na gasar. Bayani kan maƙala Marubuci, Emmanuel Akindubuwa and Isaiah Akinremi Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Sport Africa, Lagos Sa'o'i 5 da suka wuce Kyaftin din tawagar ƙwallon ƙafar Najeriya William-Troost Ekong ya ce Super Eagles na da ƙwarin guiwar yin nasara a kan Angola a gasar cin kofin Afrika ta 2023 lokacin da ƙungiyoyin za su fafata a wasan daf da na kusa da na ƙarshe a Ivory Coast. Wannan shi ne karon farko da za a yi gwagwarmaya a gasar Afcon tsakanin Najeriya da Angola, amma haɗuwar da aka yi a baya tsakanin ƙasashen na nuni da cewa wasan da za a buga a filin wasa na Felix Houphouet-Boigny da ke Abidjan. Najeriya wadda ta lashe kofin sau uku a yanzu ita ce ta ɗaya a matsayi mafi girma da ta rage a gasar bayan an yi waje da Senegal mai riƙe da kofin, da

An samu mummunar fashewa a Kenya KenyaASALIN HOTON, REUTERS

Image
Sa'o'i 2 da suka wuce Akalla mutum biyu aka tabbatar da sun mutu yayin da sama da 300 suka jikkata sakamakon wata mummunar fashewa a wata cibiyar sayar da gas din girki a Nairobi na Kenya. Cibiyar gas din na rukunin gidajen al’umma. Hotunan Bidiyon a kafafen sada zumunta sun nuna yadda wuta da hayaki suka turmuke saman rukunin benaye yayin da mutane suka shiga firgici da ruɗani domin neman tsira. Mazauna yankin Embakasi da ke kudu maso gabashin Nairobi sun ce sun ji kamar girgiza kafin ganin haske a sama a tsakar dare. Wani mazauni yankin wanda ya ce a gabansa fashewar ta auku Boniface Sifuna ya ce ta ƙyar ya tsira duk da ya samu ƙuna a jikinsa. An bayyana cewa wutar ta bazu inda ta ci gidaje da dama. Jami’an kashe gobara da jami’an agajin gaggawa sun isa wurin Kakakin gwamnatin Kenya ya ce fashewar ta faru ne a wata cibiyar da ake sayar da gas din girki. Kungiyar agaji ta Red Cross ta Kenya ta ce ta kai wasu mutane 29 da suka samu munanan raunuka zuwa babban asibitin kasar da