Muna da ƙwarin gwiwar doke Angola - Ekong
ASALIN HOTON, GETTY IMAGES Bayanan hoto, Najeriya za ta buga wasanta na 11 a matakin daf da na kusa da na ƙarshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka - babu wata ƙasa da ta kai ta buga wasanni a wannan mataki na gasar. Bayani kan maƙala Marubuci, Emmanuel Akindubuwa and Isaiah Akinremi Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Sport Africa, Lagos Sa'o'i 5 da suka wuce Kyaftin din tawagar ƙwallon ƙafar Najeriya William-Troost Ekong ya ce Super Eagles na da ƙwarin guiwar yin nasara a kan Angola a gasar cin kofin Afrika ta 2023 lokacin da ƙungiyoyin za su fafata a wasan daf da na kusa da na ƙarshe a Ivory Coast. Wannan shi ne karon farko da za a yi gwagwarmaya a gasar Afcon tsakanin Najeriya da Angola, amma haɗuwar da aka yi a baya tsakanin ƙasashen na nuni da cewa wasan da za a buga a filin wasa na Felix Houphouet-Boigny da ke Abidjan. Najeriya wadda ta lashe kofin sau uku a yanzu ita ce ta ɗaya a matsayi mafi girma da ta rage a gasar bayan an yi waje da Senegal mai riƙe da kofin, da...