Mayakan ISWAP sun kashe 'yan sanda hudu a harin da suka kai a Borno



G
NPFCopyright: NPF
Aƙalla 'yan sanda hudu ne suka rasa ransu sannan aka kwashe dimbin harsasai masu yawa a wani hari da ake zargin mayaƙan ISWAP ne suka kai ofishin 'yan sanda a Ƙaramar Hukumar Nganzai da ke Borno.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mayakan ISWAP sun kutsa kai ne cikin ofishin 'yan sandan tare da buɗe wuta kan jami'an da suke aiki.

A cewar majiyar tsaro, mahairan sun ƙona wani ɓangare na ofishin 'yan sandan lokacin da abin ya faru a ranar Juma'a.

"An samu ruɗani a garinmu a daren jiya. MMayaƙan ISWAP sun kai wa ofishin 'yan sanda hari a Gajiram. Kuma gaskiya sun fi ƙarfin jami'an da suke kan aiki."

"Mun samu gawar 'yan sanda hudu a yashe a inda abin ya faru da safiyar yau, har yanzu ba a ga wasu 'yan sandan da suka tsere ba," in ji wani jami'in 'yan sa-kai.

Rahotanni sun ce maharan sun bar wurin tun gabanin sojoji su isa.
 

Comments

Popular posts from this blog

Sojojin Najeriya sun kashe 'yan bindiga a Neja da Borno

HOTONAN Yadda Kabilar Dakarkari ke cigaba da gudanar da wasannin al'adun Gargajiya Zuru Uhola.

Babban Zauren MDD ya nemi Kwamitin Sulhu ya amince da ƙasar Falasɗinu