Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da mutane a jihar Katsina

Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da mutane a jihar Katsina

 ‘Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da mutane a jihar Katsina


Rundunar 'yan sandan jihar Katsina sun yi nasarar dakile yunkurin yin garkuwa da mutane a karamar hukumar Faskari da Malumfashi a jihar, a ranakun 8 da 9 ga watan Mayun 2024.


Kakakin rundunar 'yan sandan jihar ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya ce ‘yan bindigar sun kai harin farko ne a ranar 8 ga watan Mayu, 2024, bayan sun tare hanyar Funtua zuwa Gusau, a kauyen Unguwar Boka, a karamar hukumar Faskari.


A cewarsa, ‘yan ta’ad-dan sun far wa fasinjojin da ke tafiya a cikin wata kirar motar Golf III, inda suka ci da halbe-halbe.


Sai dai Sadiq ya bayyana cewa shirin nasu ya ci tura sakamakon wani dauki da jami’an sintiri suka kai.


Daily news hausa

Comments

Popular posts from this blog

Sojojin Najeriya sun kashe 'yan bindiga a Neja da Borno

HOTONAN Yadda Kabilar Dakarkari ke cigaba da gudanar da wasannin al'adun Gargajiya Zuru Uhola.

Babban Zauren MDD ya nemi Kwamitin Sulhu ya amince da ƙasar Falasɗinu