ASALIN HOTO Rundunar sojin Najeriya ta ce ta dakarunta sun samu nasarar kashe 'yan bindiga da dama a jihohin Borno da Neja. Cikin wata sanarwar da mai magana da yawun rundunar sojin saman ƙasar, Edward Gabkwet ya ce cikin jerin wasu hare-hare ta sama da dakarun rundonin Hadin Kai da Whirl Punch suka ƙaddamar a jihohin biyu ya samu narasar lalata wasu shirye-shiryen 'yan bindigar. Edward Gabkwet ya ce a ranar 3 ga watan Mayu dakarun ƙasar sun kai hari a garin Chinene da ke yankin tsaunin Mandara da ke kusa da jihar Borno. Ya ce dakarun sojin ƙasar sun ga 'yan bindigar na wani taro da ake kyautata zaton tattaunawa suke yi a lokacin da jirgin sojin ya kai musu hari tare da kashe su. “Haka kuma a garin sojojinmu sun hangi wasu motocin yaƙi bakwai da ake zaton na 'yan bindigar ne a ƙarƙashin wata bishiya, nan take su ma aka kai musu hari tare da lalata su'', in ji sanarwar. Sanarwar ta ƙara da cewa “bayanan da muka samu bayan hare-haren sun nuna cewa an samu nasara...
HOTONAN Yadda Kabilar Dakarkari ke cigaba da gudanar da wasannin al'adun Gargajiya Zuru Uhola. Bikin raya al'adun Gargajiya na kabilar Dakarkari dake masarautar Zuru a jihar kebbi biki ne da ake gudanarwa domin nuna godiya ga Allah. Dubban al'umma ne ciki da wajen jihar suka halarci taron ciki hadda dan majalisar tarayyar Najeriya mai wakiltar masarautar Zuru Hon Kabir Ibrahim Tukura. Hoto📷 Abbakar Aleeyu Anache
Copyright: Reuters BABAN zauren Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi ƙira ga Kwamitin Sulhu na Majalisar da ya tabbatar da 'yancin Falasɗinawa ta hanyar amincewa da kasar a matsayin mamba a majalisar. Falasɗinu dai na da matsayin ƙasa 'yar sa ido tun shekarar 2012, wani abu da ke nuna rashin cikakken 'yancinta na kasancewarta ƙasa mai 'yancin a zauren. Kwamitin Tsaro na Majalisar ta Dinkin Duniya ne kawai yake da damar tabbatar da hakan. Amurka za ta hau kujerar naƙi dangane da zaman Falasɗinu samun matsayin zaman cikakkiyar mamba a kwmaitin. To sai dai zaɓen na ranar Juma'a ya nuna irin goyon bayan da ake nuna wa ƙasar Falasɗinawa. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasashen Turai ke ƙoƙarin amincewa da ƙasar Falaɗinawa.
Comments