Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai buɗe taron yaƙi da ta'addanci na Afirka da za a gudanar a Abuja fadar gwamnatin ƙasar. Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban na Najeriya, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce taron - wanda Najeriya da haɗin gwiwar ofishin yaƙi da ta'addanci na Majalisar Dinkin Duniya suka shirya - za a fara shi ranar Litinin 22 ga watan Afrilu. Manufar taron ita ce ƙarfafa haɗin gwiwa don yaƙi da ta'addanci a ƙasashen Afirka tare da sake fasalin yadda duniya ke kallon ta'addanci a Afirka, da kuma lalubo sabbin hanyoyin magance matsalar a faɗin nahiyar. Ana sa ran shugabannin gwamnatoci da manyan jami'an gwamnatocin ƙasashen Afirka, da wakilan ƙungiyoyin duniya da cibiyoyi, da jami'an diplomasiyya da ƙungiyoyin fararen hula za su halarci taron. Sanarwar ta ƙara da cewa ana sa ran mataimakiyar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed za ta halarci taron. ''Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro Malla...
Copyright: Other Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta fara gudanar da bincike kan al’amarin da ya biyo bayan zargin fille kan wani karamin yaro ɗan shekara shida da wani almajiri ya yi a kauyen Kanwa da ke karamar hukumar Madobi. Rahotanni dai sun nuna cewa almajirin mai shekaru 22 ya kashe yaron ne a kusa da wata makarantar firamare kafin ya cire kansa. Kwamishinan 'yan sandan jihar, CP Usaini Gumel ya shaida wa BBC cewa almajirin bayan ya yanke wa yaron kai ya jefa da kan a cikin wani masai. "A jiya ne aka wayi gari da wannan labari da ke cewa wasu masu ruwa da tsaki suka lura da cewa sun ga wani yaro a wannan ƙauye da wuƙa wanda suka ga alamun jini a jikin wuƙar kamar jinin ɗan Adam ne, Hakan ne ya sa suka zarge abin da ya sa 'yan unguwa suka cafke shi, suka tasa shi gaba, sai suka ga gangar jikin mutum inda ya amsa shi ne ya kashe shi. Bayan da ƴan sanda suka je, shi ne ya ja su ya kai su inda ya wurgar da kan, inda suka ga kan yaron." In ji kwamishinan 'ya...
a matsayin Mai bashi shawara akan harkokin matasan da wasanni tare da wasu mutum takwas Wanda zasu taimakawa Gwamnan a fanno daban daban . A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, a Wanan Rana yace Gwamnan ya amince da nada 1. Farfesa Ibrahim Magaji Barde, a matsayin mai bashi shawara na musamman kan harkokin tattara kudaden shiga (IGR). 2. Dr. Abdulhamid Danladi, mai bashi shawara na musamman kan harkokin kasashen waje II 3. Engr. Bello Muhammad Kiru, mai bashi shawara na musamman kan albarkatun ruwa. 4. Yusuf Shuaibu Imam (Ogan Boye) ya sake nada shi a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin matasa da wasanni. 5. Dr. Nura Jafar Shanono an dauke shi daga mai ba da shawara na musamman kan albarkatun ruwa zuwa Manajan Darakta, a ma.aikatar Ruwa da Gine-gine (WRECA). 6.Haka kuma Baba Abubakar Umar ya samu sauyi daga mai bawa gwamna Kano shawara na musamman ga harkokin makarantu mas...
Comments