Tinubu zai jagoranci taron yaƙi da ta'addanci na Afirka a Abuja

Tinubu zai jagoranci taron yaƙi da ta'addanci na Afirka a Abuja

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai buɗe

 taron yaƙi da ta'addanci na Afirka da za a gudanar a Abuja fadar gwamnatin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban na Najeriya, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce taron - wanda Najeriya da haɗin gwiwar ofishin yaƙi da ta'addanci na Majalisar Dinkin Duniya suka shirya - za a fara shi ranar Litinin 22 ga watan Afrilu.

Manufar taron ita ce ƙarfafa haɗin gwiwa don yaƙi da ta'addanci a ƙasashen Afirka tare da sake fasalin yadda duniya ke kallon ta'addanci a Afirka, da kuma lalubo sabbin hanyoyin magance matsalar a faɗin nahiyar.

Ana sa ran shugabannin gwamnatoci da manyan jami'an gwamnatocin ƙasashen Afirka, da wakilan ƙungiyoyin duniya da cibiyoyi, da jami'an diplomasiyya da ƙungiyoyin fararen hula za su halarci taron.

Sanarwar ta ƙara da cewa ana sa ran mataimakiyar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed za ta halarci taron.

''Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu, da sakataren sashen yaƙi da ta'adancin na Majalisar Dinkin Duniya, Vladimir Voronkov, za su gabatar da jawabai a wurin taron'', kamar yadda sanarwar ta yi bayani.

Comments

Popular posts from this blog

An ga watan Azumin Ramadan a Saudiyya

Yadda wani almajiri ya fille wa ɗan shekara shida kai a Kano